Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2005-04-12 10:28:37    
Gwamnatin Cote d'Ivoire ta musanta labarin kai farmaki ga dakarun adawa da gwamnatin

cri
Ran 11 ga wannan wata gwamnatin kasar Cote d'Ivoire ta musanta sanarwar da tsohon dakarun adawa da gwamnati (wato the New Forces) na yanzu ya bayar, kan wai askarawan sojojin gwamnatin kasar za su kai masa hari.

Wani mashawarci kan harkokin tsaron kasar na shugaban kasar Cote d'Ivoire ya bayyana a ran nan cewa, sanarwar da dakarun New Forces ya bayar a ran 10 ga watan nan, wai cewa rundunar sojin gwamnatin kasar tana daukar sojojin haya da kuma yin shirin kai masa hari, ko kusa ba shi da kan gado. A sa'i daya kuma ya yi suka kan dakarun New Forces saboda sun nemi cin amanar yarjejeniyar zaman lafiya da bangarori daban daban na kasar Cote d'Ivoire suka rattaba hannu a kai a birnin Pretoria a kwanan baya.(Tasallah)