
Ran 7 ga wata, jami'in kiyaye zaman lafiya na kasar Senegal ya yi gargadi cewa, yanzu cutar kaalara ta fara yaduwa a kasar Senegal.
Bisa kididdigar da aka yi, a cikin kwanaki 10 a baya, an sami mutane masu gamu da cutar 3,700, mutane 50 da ke cikinsu sun riga sun je gidan gaskiya. Yanzu kwalara ta fara yaduwa daga birnin Touba na kasar Senegal zuwa kasashen makwabcinta. Makwabcinta kasar Gambia ta riga ta sami mutane 12 sun gamu da cutar, kuma 2 da ke cikinsu sun mutu.
Bisa labarin da muka samu, Senegal ta riga ta kafa kwamitin yaki da cutar kwalara don kai farmaki ga cutar.
|