Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2005-04-01 10:39:37    
Mr.Annan ya nuna maraba ga dakarun 'yantar da ruwanda da su kwance damara

cri
A ran 31 ga wata, babban sakataren MDD Kofi Annan ya bayar da wata sanarwa, inda ya nuna maraba ga dakarun da ba su ga maciji da gwamnatin Ruwanda, wato dakarun 'yantar da Ruwanda, da su yi shelar kwance damara bisa son ransu.

A cikin sanarwar, an kuma sa kaimi ga gwamnatocin kasashen Congo Kinshasa da Ruwanda da su dauki mataikai kamar yadda ya kamata, don tabbatar da komawar dakarun nan a Ruwanda lami lafiya. Ban da wannan, an kuma nemi dakarun musamman na MDD a kasar Congo Kinshasa da su ba da taimako.

A ran nan kuma, a birnin Rome na Italiya, dakarun 'yantar da Ruwanda sun bayar da sanarwar cewa, suna son gama yakin da suke yi da gwamnatin Ruwanda, su kwance damara, kuma su koma Ruwanda.(Lubabatu Lei)