Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2005-03-31 09:23:14    
Shugaba Mugabe ya yi kira ga kasashen duniya da su martaba zabin da jama'ar kasar Zimbabwe za su yi

cri

Shugaba Mugabe na kasar Zimbabwe ya yi nuni da cewa, tabban ne, Jam'iyyar Hadin Al'umma da Kaunar Kasa ta Afirka ta ZANU-PF wadda ke rike da ragamar mulki a kasar za ta ci nasara a wajen zaben 'yan majalisar dokoki da za a yi a ran 31 ga wata. Har wa yau kuma, ya yi kira ga kasashen duniya da su martaba zabin da jama'ar kasar Zinbabwe za su yi.

Ran 30 ga wata, a garin Glen Norah da ke kudu maso yammacin lardin Harare, Jam'iyyar ZANU-PF ta yi taro na karshe kafin zaben da za a yi, inda shugaba Mugabe ya yi wannan bayani. Ya ce, idan jam'iyyar ZANU-PF ta ci zaben, to, kamata ya yi, wanda ya fadi a takarar ya nuna girmamawa ga sakamakon zaben, bai kamata ba ya matsa wa mai cin zabe lamba tare da goyon bayan da kasashen waje suka bayar. (Bello)