Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2005-03-17 09:53:47    
Mutane 40 sun mutu a sakamakon gocewar kasa ta wani ramin haka lu'ulu'u a kasar Kongo(Kinshasa)

cri
A ran 16 ga wata shugaban jihar Kasai Occidental na kasar Kongo(Kinshasa) Clement Kantu ya bayyana cewa, a kwanakin nan, an sami gocewar kasa cikin wani ramin haka lu'ulu'u na jihar, wanda ya yi sanadiyyar mutuwar mutane a kalla 40.

Bisa labarin da muka samu, an ce, wannan rami yana iyakar kasa da ke tsakanin kasashen Kongo(Kinshasa) da Angola, kuma an yi hadarin ne a karshen watan Fabrairu na wannan shekara, sabo da na'urorin sadarwa da zirga-zirga su ba na zamani ba ne, shi ya sa bayan da aka yi hadarin da rabin wata, sa'an nan mutanen da ke birnin Kinshasa, babban birnin kasar sun sami labarin. Bisa labarin da muka samu, an ce, an yi wannan hadari ne a sakamakon hakar lu'ulu'u da aka yi ba bisa doka ba.(Danladi)