Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2005-03-16 18:13:08    
Annobar sankarau ta bulla a yankin arewa maso gabashin kasar Cote dI'voire

cri
A 'yan kwanakin nan annobar sankarau tana yaduwa sosai a yankin arewa maso gababashin kasar Cote dI'voire, wadda har ta yi sanadiyyar mutuwar mutane fiye da 30 da suka kamu da ciwon. Sabo da haka, kungiyar kiwon lafiya ta kasa da kasa tana mai da hankali sosai kan wannan.

A ran 15 ga wata, ofishin wakilin kungiyar kiwon lafiya ta kasa da kasa da ke kasar Cote dI'voire ya tabbatar da cewa, a yankin Bunna na kasar Cote dI'voire da ke iyaka da kasar Burkina Faso an riga an gano masu ciwon sankarau 168. Mutane 37 daga cikinsu sun riga sun mutu. Sabo da haka, ma'aikatar kiwon lafiya ta kasar Cote dI'voire tana da shirin tura wasu likitoci zuwa yankin domin yin rigakafi da hana yaduwar annobar ciwon. (Sanusi Chen)