Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2005-03-16 10:17:18    
Kasar Nijeriya za ta ci gaba da neman samun kujerar din din din ta kwamitin sulhu ta Majalisar Dinkin Duniya

cri

Shugadan Nijeriya Olusegun Obasanjo

Ministan harkokin wajen kasar Nijeriya Olu Adeniji ya bayyana a birnin Abuja, hedkwatar kasar a ran 16 ga wannan wata cewa, kasarsa za ta ci gaba da neman samun kujerar din din din ta kwamitin sulhu ta Majalisar Dinkin Duniya.

Mr. Adeniji ya kara da cewa, a kwanan baya, mambobin kwamitin zartaswa na Kawancen Kasashen Afirka sun riga sun sami ra'ayi daya kan matsayin da kasashen Afirka za su dauka a kan yin gyare-gyaren kwamitin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya, wato sun bukaci majalisar da ta bayar da a kalla kujerun din din din guda 2 na kwamitin sulhu ga kasashen Afirka. Kasarsa za ta yi kokarin neman samun daya daga cikin wadannan kujeru 2, bisa shirin da abin ya shafa da Kawancen Kasashen Afirka ya gabatar.(Tasallah)