Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2005-03-02 09:06:57    
An kama shugaban sojojin kabila na kasar Kongo(Kinshasa) wadan ake tuhumarsa da laifin kai farmaki ga sojojin kiyaye zaman lafiya na MDD

cri
A ran 1 ga wata da yamma, wakilin musamman na babban sakataren MDD da ke kasar Kongo(Kinshasa) ya bayyana cewa, an riga an kama shugaban sojojin kabila na kasar Kongo(Kinshasa) wanda ake tuhumarsa da laifin kai farmaki ga sojojin kiyaye zaman lafiya na MDD.

Bisa labarin da muka samu daga tawagar musamman ta MDD da ke kasar Kongo(Kinshasa), an ce, bi da bi ne gwamnatin kasar Kongo(Kinshasa) da sojojin kiyaye zaman lafiya na MDD suka dauki matakan cafke shi a shiyyoyin Kinshasa da Ituri, sojojin kiyaye zaman lafiya na MDD sun gamu da dagiya daga dakarun kabilar wurin. Amma tawagar musamman ta MDD da gwamnatin kasar Kongo(Kinshasa) ba su fayyace yawan wadanda aka kama su da asalinsu ba.(Danladi)