Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2005-02-25 17:11:26    
Madam Chen Zhili ta gana da jami'an kasar Tanzania

cri
A ran 25 ga wannan wata, a nan birnin Beijing, hedkwatar kasar Sin, wakiliyar majalisar gudanarwa ta kasar madam Chen Zhili ta gana da kungiyar wakilan al'adu ta kasar Tanzania wadda ke yin ziyara a nan.

A lokacin ganawar da ta yi, madam Chen ta bayyana cewa, gwamnatoci da jama'ar kasashen nan 2 suna da abokantaka ta gargajiya da ingantacciyar huldar hadin gwiwa da sada zumunci a tsakaninsu. Dukan shugabannin kasashen nan 2 na da da na yanzu sun dora muhimmanci sosai kan dangantakar da ke tsakanin kasashen nan 2, bayan da aka kafa huldar diplomasiyya a tsakaninsu, kasashen Sin da Tanzania sun yi ta yin mu'amala da hadin gwiwa a fannonin al'adu da aikin ba da ilmi, a sakamakon haka, sun kara fahimtar juna da zurfafa zumuncin da ke tsakaninsu.(Tasallah)