Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2005-02-25 13:49:34    
An samu bazuwar cutar kwalara a kasar Nijeriya wadda ta kashe a kalla mutane 46

cri

Ran 24 ga wata, wani jami'in kasar Nijeriya ya tabbtar da cewa, cikin makonni 2 da suka wuce, cutar kwalara da ke brbazuwa a jihar Oyo ta kudu maso yammacin kasar Nijeriya ta yi sanadiyyar mutuwa a kalla mutane 46.

Bisa labarin da jimi'in nan ya bayar, an ce, wurin da aka samu bazuwar annoba shi ne yankin Kusa da ke dab da birnin Ibadan, fadar gwamnatin jihar Oyo, kuma yawancin mazaunan masu haka ma'adinan da ke karkashin kasa ne. Bisa binciken da aka yi, an ce, dalilin da ya haifar da annoba shi ne gurbacewar ruwan sha. Yanzu ban da mutane 46 wadanda suka riga mu gidan gaskiya, akwai wasu fiye da 100 suna cikin asibiti sabo da cutar. (Bello)