Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2005-02-22 10:02:43    
Gwamnatin Kongo Kinshasa ta girke 'yan sanda a arewa maso gabashin kasar a karo na farko bayan shekaru 8 da suka wuce

cri

Ran 21 ga wata, 'yan sanda 300 na kasar Jamhuriyar Dimokuradiyya ta Kongo sun fara aikinsu a birnin Bunia, fadar gwamnatin yankin Ituri da ke arewa maso gabashin kasar. Wannan karo na farko ne da gwmnatin kasar ta girke 'yan sanda a yankin bayan shekaru 8 da suka wuce.

A daidai wannan rana, Theophile Mbemba, ministan kasar mai kula da harkokin gida ya ba da jawabi, inda ya yi kira ga jama'a da masu mukami da ke yankin da su yi kokari domin wanzar da sulhuntawa da zaman lafiya a tsakanin kabili dabam daban. Ya ce, kamata ya yi, mutane miliyan 6 da ke zaune a yankin Ituri wanda fadinsa ya kai muraba'in kilomita dubu 65, su yi zamansu cikin lumana, kuma su yi amfani da albarkacin kasar da Allah ya fuwace yankin domin raya kansu. (Bello)