Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2005-02-04 09:08:07    
Nelson Mandela ya yi kira ga kasashe masu wadata da su ba da taimako ga kasashe masu talauci

cri
A ran 3 ga wata, a birnin London, tsohon shugaban kasar Afirka ta Kudu Nelson Mandela wanda ke yin ziyara a kasar Ingila, ya yi kira ga kasashe masu wadata da su ba da taimako ga kasashe masu talauci don kubutar da su daga mawuyacin hali.

Mr.Mandela ya yi kira ne a gun wani biki mai suna "mayar da talauci don ya zamo tarihi" da aka shirya a London. hakan nan kuma yana fatan kasashe masu sukuni za su dauki matakai tun da wuri, ta yadda za a kubutar da matalauta miliyoyi na duk duniya daga talauci.

A ran 4 ga wata kuma,, Mr.Mandela zai halarci taron ministocin kudi na kasashen yamma 7 da za a yi a London, inda kuma zai bayar da jawabi, don yin kira ga ministocin kudi na kasashe masu sukuni da su kara ba da taimako ga kasashe masu tasowa wajen daidaita matsalar talauci.(Lubabatu Lei)