Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2005-01-28 15:32:27    
Mataimakin babban sakatare na majalilsar dinkin duniya ya nemi a sa lura ga hadarin mutuntaka na kasashen Afrika

cri
Labarin da aka kawo mana ya bayyana cewa, a ran 27 ga watan nan da muke ciki, a gun taron tattauna halin mutuntaka na kasashen Afrika da kwamitin sulhu na majalisar dinkin duniya ya shirya, Mr.Jan Egeland mataimakin babban sakatare na majalisar dinkin duniya ya nemi kasashen duniya da su sa lura sosai ga hadarin mutuntaka na kasashen Afrika.

Mr.Egeland ya ce, majalisar dinkin duniya tana tafiyar da aikin ba da taimako a kasar Sudan da Congo Kinshasha da sauran kasashen Afrika cikin dogon lokaci,amma tana gamu da matsalar karancin kudi, ya kamata kasashen duniya sun ba da taimako ga wadannan kasashen dake shan wahalar karancin kudi kamar yadda suka yi kan kasashen dake gabar tekun Indiya.Wato za su ba da taimako ga masu shan wahalar yake yake da yunwa da ciwace ciwace.(Dije)