Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2005-01-28 11:04:30    
Ana sa ran cewa za a samu babbar nasara wajen kau da talauci a Afrika, in ji Mista Blaire

cri

Ran 27 ga watan nan, Tony Blaire, firayin ministan kasar Birtaniyya, wanda ke halartar taron shekara-shekara na dandalin tattalin arzikin duniya da ake yi a birnin Davos na Switherland, ya yi nuni da cewa, kasar Birtaniyya za ta yi amfani da kafar zaman kasar da ke shugabancin karba-karba ta rukunin kasashe 8, domin neman samun sahihan cigaba wajen kau da talauci a kasashen Afrika.

Mista Blaire ya ce, wahalolin da jama'ar Afirka ke fama da su a cikin zamansu na yau da kullum sun fi tunanin mutane. Shi ya sa, zai yi kokari tare da shugabannin kasashen Afrika domin daukar matakan bayar da taimako ga jama'ar Afrika wajen yakar talauci. Ban da wannan kuma, ya yi nuni da cewa, kasar Birtaniyya za ta kara bayar da kudin Ingila Fam miliyan 25 domin aikin ragakafin cutar malariya a Afrika. (Bello)