Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2005-01-28 10:26:19    
Ana mai da hankali kan talaucin da ake fama da shi a Afrika a gun dandalin tattalin arziki na duniya

cri

Ran 27 ga watan, a gun dandalin tattalin arziki da ake yi a birnin Davos na Switherland, an yi tattaunawa kan batun Afrika, masu halartar taron sun yi kira ga kasashen duniya da su mai da hankali kan halin kaka-nika-yi da ake ciki a Afrika, da kuma dauki matakai domin neman kawar da talauci a wurin.

Shugaba Obasanjo na kasar Nijeriya ya nuna cewa, game da kasashen Afrika, samun bunkasuwa ya fi neman taimako muhimmanci. Ya kamata a yi cinikayyar kasa da kasa cikin adalci, ta yadda za a inganta tattalin arzikin kasashen Afrika.

Shugaba Mbeki na kasar Afrika ta Kudu ya yi nuni da cewa, babban aikin kungiyar kawancen kasashen Afrika shi ne tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a Afrika, domin sai dai a cikin halin lumana ne za a samu bunkasuwa.(Bello)