Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2005-01-27 10:18:49    
Kasar Guinea-Bissau za ta kira taron kasa da kasa domin tattara kudi

cri

Ran 26 ga wata, wani jami'in kasar Guinea-Bissau ya tabbatar da cewa, farkon watan mai zuwa, Carlos Gomes Junior, firayin ministan kasar zai kira wani taron kasa da kasa, inda za a bukaci kasashen mahalartar taron da su bayar da taimako ga gwamnatin kasar Guinea-Bissau, yadda za a fid da shi daga cikin mawuyancin hali na rashin kudi.

Bisa labarin da muka samu, za a yi taron a birnin Lisbon, fadar mulkin kasar Potugal. Potugal da Faransa sun nuna goyon baya ga gwamnatin kasar Guinea-Bissau da ta yi wannan taron.

Bisa bayanin da jami'in ya yi, an ce, a wannan shekarar da muke ciki, gibin kudin da aka samu a cikin kasafin kudin gwamnatin kasar Guinea-Bissau ya kai kudin Amurka miliyan 84. Ban da wannan kuma, kasar tana bukatar kudin taimako dalar miliyan 5, domin shirya babban zaben da za a yi a watan Mayu mai zuwa. (Bello)