Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2005-01-07 18:09:21    
Mataimakin shugaban kasar Nijeriya zai hallarci bikin kulla yarjejeniyar shimfida zaman lafiya a kasar Sudan

cri
A madadin shugaban kasar Nijeriya kuma shugaban kawancen kasashen Afirka ne, mataimakin shugaban kasar Nijeriya Atiku Abubakar zai tashi daga kasar a ranar Asabar zuwa birnin Nairobi, inda shi da sauran shugabannin kasashen duniya za su hallara a gun bikin sa hannu a kan yarjejeniyar shimfida zaman lafiya ta sa ayar yakin basasa da aka shafe shekaru 21 ana yinsa a tsakanin gwamnati da 'yan tawaye, wato kungiyar 'yantattar da jama'a ta kasar Sudan. Za a yi wannan biki ne a ranar Lahadi, wato ran 9 ga watan nan a Nairobi babban birnin kasar Kenya.

Kamfanin dillanci labaru na Nijeriya ne ya yada wannan labari a ran 6 ga watan nan.

A watan Mayu na shekarar bara, gwamnatin Sudan da 'yan tawayen da ke kudancin kasar sun riga sun kai ga daddale yarjejeniyoyin 6 domin kawo zaman lafiya a tsakaninsu, yarjejeniyoyin sun shafi wasu muhimman matsalolin raba ikon gwamnati da yadda za a yi mulkin yankuna 3 a cikin kwarya-kwaryar tsawon lokaci na shekaru 6 masu zuwa. Ban da wannan, a ran 31 ga watan Disamba na shekarar bara, sun sami ra'ayi daya kan wata muhimmiyar matsala daban da ta kasance a tsakaninsu. (Sanusi Chen)