|
 |
 |
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye | more>> |
|
 |
|
 |
|
|
 |
(GMT+08:00)
2005-01-07 17:07:51
|
A fili ne shugaban kasar Cote D'ivoir ya gabatar da manyan ayyuka guda hudu na gwamnati
cri
Labarin da aka kawo mana ya bayyana cewa, a ran 6 ga watan nan da muke ciki, a gun taro na majalisar ministoci na karo na farko na shekara ta 2005, a fili ne shugaba Laurent Gbagbo na kasar Cote D'ivoir ya gabatar da manyan ayyuka guda hudu na gwamnati na yanzu, inda ya nemi gwamnati da ta dauki matakai don neman shimfida zaman lafiya a duk kasa.
Wadannan manyan ayyuka guda hudu na gwamnati sun hada da kwance damara ga dakaru da sake tafiyar da ayyukan kulawa da yin share fage ga babban zaben da za a yi a watan October na shekarar 2005 da sake gina mahaifar Cote D'ivoir.(Dije)
|
|
|