Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2005-01-06 09:54:45    
Masar ta musunta labarin da aka bayar wai ta taba yin gwajin makaman nukiliya

cri

Ran 5 aga watan nan, Ahmed Abul Gheit, ministan harkokin waje na kasar Masar ya bayar da wata sanarwa, inda ya musunta labarin da wasu kamfanonin watsa labaru na kasashen yamma suka bayar wai kasar Masar ta taba yin gwajin makaman nukiliya a cikin asiri bayan ta sa hannu kan yarjejeniyar hana yaduwar makaman nukiliya.

Mista Abul Gheit ya ce, an rubuta labarin ba bisa tushen gasakiya ba, kasar Masar tana bin yarjejeniyar hana yaduwar makaman nukiliya sosai.

Yayin da ake musunta labarin, gwamnatin kasar Masar ta jaddada cewa, ta gudanar da shirinta na nukiliya ne domin bayar da wutar lantarki, ba wai domin kera makmai ba. (Bello)