Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2004-12-14 09:32:09    
Kasar Sin tana fatan kasar Sudan za ta iya daidaita matsalar da take fama da ita yanzu da kanta

cri
A ran 13 ga wata a nan birnin Beijing, wakilin majalisar gudanarwa ta kasar Sin Zhou Yongkang ya bayyana cewa, kasar Sin tana fatan kasar Sudan za ta iya yin kokari kan daidaita matsalar da take fama da ita yanzu da kanta, kuma za ta iya cimma burin raya tattalin arziki da sulhuntar siyasa.

Mr. Zhou ya fadi haka ne lokacin da yake ganawa da kungiyar wakilan kasar Sudan wadda ke karkashin jagorancin malam Awad Ahmed Al-Jaz, wato ministan makamashi da albarkatun halittu na kasar Sudan.

Mr. Zhou ya kuma bayyana farin cikinsa ga dangantakar dake tsakanin kasar Sin da kasar Sudan. Ban da wannan, Mr. Zhou ya tabbatar da sakamakon da kasashen nan biyu suka samu a fannoni daban-dabam.

Malam Al-Jaz ya kuma gode wa gwamnatin kasar Sin domin ta nuna goyon baya ga bunkasuwar tattalin arziki da zaman al'ummar kasar Sudan a cikin dogon lokacin da ya gabata. Malam Al-Jaz ya kuma yi fatan lokacin da ake gaggauta ayyukan shimfida zaman lafiya a kasar Sudan, za a iya bude sabbin fannonin hadin guiwa a tsakanin kasashen nan biyu. (Sanusi Chen)