Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2004-11-20 17:12:11    
Kwamitin sulhu na Majalisar Dindin duniya ya zartas da kuduri a kan batun kasar Sudan

cri
Ran 19 ga wata, an rufe taron musamman na kwamitin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya kan batun kasar Sudan wanda aka shafe kwanaki biyu ana yinsa a birnin Nairobi, hedkwatar kasar Kenya. A gun taron, an zartas da kuduri don neman bangarori biyu masu gwabzawa da juna na kudancin kasar Sudan da su daddale yarjejeniyar zaman lafiya ta karshe a tsakaninsu tun da wurwuri.

A wannan rana, a birnin Nairobi, gwamnatin kasar Sudan da kungiyar kwatar 'yancin jama'ar Sudan wadda ke yin adawa da gwamnati a kudancin kasar sun sa hannu a kan takardar tabbatar da tsagaita bude wuta, kuma sun dauki alkawari cewa, bangarorin nan biyu za su kulla yarjejeniyar daina yakin basasa da aka shafe shekaru 21 ana yinsa a kasar Sudan kafin ran 31 ga watan gobe. Mr Amr Mussa, babban sakataren Kawancen Kasashen Larabawa ya bayar da sanarwa a birnin Alkahira don yin maraba da wannan. (Halilu)